• Home
  • Agric
  • Sci & Tech
  • Health
  • Environment
  • Hausa News
  • More
    • Business/Banking & Finance
    • POLITICS
    • Entertainments & Sports
    • International
    • Investigation
    • Law & Human Rights
    • Africa
    • ACCOUNTABILITY/CORRUPTION
    • Hassan Gimba
    • Column
    • Prof. Jibrin Ibrahim
    • Prof. M.K. Othman
    • Defense/Security
    • Education
    • Energy/Electricity
    • Entertainment/Arts & Sports
    • Society and Lifestyle
    • Food & Agriculture
    • Health & Healthy Living
    • International News
    • Interviews
    • Investigation/Fact-Check
    • LAW & HUMAN RIGHTS
    • Oil & Gas/Mineral Resources
    • PRESS FREEDOM/JOURNALISM/PR
    • General News
    • Presidency
  • About Us
    • Contact Us
    • Board Of Advisory
    • Privacy Policy
    • Ethics Policy
    • Teamwork And Collaboration Policy
    • Fact-Checking Policy
    • Advertising
  • Media OutReach Newswire
    • Wire News
  • The Stories
Facebook Twitter Instagram
Trending
  • Naira ends June at ₦1,376/$ despite mid-month swings
  • World Bank approves $1.25bn loan for Nigeria despite public criticism
  • Lagos urges residents to remain calm as flooding persists, approves dredging of 28 drainage channels
  • ADC, 8 other political parties obtain INEC access codes for upload of 2027 candidates [LIST]
  • FG to launch 3 new digital platforms for MDA reforms on July 14
  • APC submits final senatorial candidates to INEC, replaces Suswam, others [NAMES]
  • Kano targets zero maternal mortality in 4 years
  • Zamfara govt earmarks N7.2bn for projects in 375 communities
Facebook Twitter Instagram YouTube
AsheNewsAsheNews
  • Home
  • Agric

    Experts advise farmers on flood prevention measures

    June 30, 2026

    Japan donates $853,000 food aid to ease hunger crisis in Northeast Nigeria

    June 30, 2026

    Lagos fruit traders improvise to beat spoilage, high storage costs

    June 30, 2026

    Plateau farmers appeal for fertiliser subsidy

    June 30, 2026

    Abia partners with FG to combat Tse-tse flies, pests

    June 30, 2026
  • Sci & Tech

    NCC urges accelerated FTTH deployment to achieve $1tn economy

    July 1, 2026

    WhatsApp rolls out username reservations for better privacy

    June 29, 2026

    FG to launch digital education data system July 1

    June 29, 2026

    Radiant diGiLog unveils all in one workforce management platform

    June 29, 2026

    MRTBN registrar calls for better funding, more physiotherapists

    June 27, 2026
  • Health

    Kano targets zero maternal mortality in 4 years

    July 1, 2026

    Okeniyi calls for increased investment in paediatric cardiac care

    July 1, 2026

    Audiologist warns against prolonged earphone use

    June 30, 2026

    Stay in Nigeria, build your career, new doctors urged

    June 30, 2026

    eHealth Africa strengthens partnerships for digital health solutions

    June 30, 2026
  • Environment

    Lagos urges residents to remain calm as flooding persists, approves dredging of 28 drainage channels

    July 1, 2026

    FG to launch 3 new digital platforms for MDA reforms on July 14

    July 1, 2026

    Zamfara govt earmarks N7.2bn for projects in 375 communities

    July 1, 2026

    REDAN urges Wike to review Abuja master plan without touching parks

    June 30, 2026

    NIWA, NEMA strengthen collaboration on flood preparedness

    June 30, 2026
  • Hausa News

    UNA signs MoU to launch air Bissau in Guinea-Bissau

    June 15, 2026

    Otti plans 250-room 5-star hotel in Umuahia

    April 11, 2026

    Anti-quackery task force seals 4 fake hospitals in Rivers

    August 29, 2025

    [BIDIYO] Yadda na lashe gasa ta duniya a fannin Ingilishi – Rukayya ‘yar shekara 17

    August 6, 2025

    A Saka Baki, A Sasanta Saɓani Tsakanin ‘Yanjarida Da Liman, Daga Muhammad Sajo

    May 21, 2025
  • More
    1. Business/Banking & Finance
    2. POLITICS
    3. Entertainments & Sports
    4. International
    5. Investigation
    6. Law & Human Rights
    7. Africa
    8. ACCOUNTABILITY/CORRUPTION
    9. Hassan Gimba
    10. Column
    11. Prof. Jibrin Ibrahim
    12. Prof. M.K. Othman
    13. Defense/Security
    14. Education
    15. Energy/Electricity
    16. Entertainment/Arts & Sports
    17. Society and Lifestyle
    18. Food & Agriculture
    19. Health & Healthy Living
    20. International News
    21. Interviews
    22. Investigation/Fact-Check
    23. LAW & HUMAN RIGHTS
    24. Oil & Gas/Mineral Resources
    25. PRESS FREEDOM/JOURNALISM/PR
    26. General News
    27. Presidency
    Featured
    Recent

    Naira ends June at ₦1,376/$ despite mid-month swings

    July 1, 2026

    World Bank approves $1.25bn loan for Nigeria despite public criticism

    July 1, 2026

    Lagos urges residents to remain calm as flooding persists, approves dredging of 28 drainage channels

    July 1, 2026
  • About Us
    1. Contact Us
    2. Board Of Advisory
    3. Privacy Policy
    4. Ethics Policy
    5. Teamwork And Collaboration Policy
    6. Fact-Checking Policy
    7. Advertising
    Featured
    Recent

    Naira ends June at ₦1,376/$ despite mid-month swings

    July 1, 2026

    World Bank approves $1.25bn loan for Nigeria despite public criticism

    July 1, 2026

    Lagos urges residents to remain calm as flooding persists, approves dredging of 28 drainage channels

    July 1, 2026
  • Media OutReach Newswire
    • Wire News
  • The Stories
AsheNewsAsheNews
Home»General News»[RA’AYI)] Adawar Siyasa A Jihar Sokoto Da Sauran Lamurra
General News

[RA’AYI)] Adawar Siyasa A Jihar Sokoto Da Sauran Lamurra

EditorBy EditorSeptember 6, 2024Updated:September 6, 2024No Comments5 Mins Read
Sokoto-state-map
Share
Facebook Twitter LinkedIn Pinterest Email

Haƙiƙa lamarin jagorancin jama’a a lokacin dimokraɗiyya yana tafiya ne da adawa. Sai dai kuma idan za a yi adawar, ya dace a yi mai ma’ana wadda hankali ke ɗauka. Lallai an yi adawa a lokacin gwamnatin Alhaji Attahiru Ɗalhatu Bafarawa ta APP/ANPP (1999-2003) inda a lokacin, su Hon. Abubakar Shehu Tambuwal da Hon. Arzika Tureta (marigayi) suke a sahun gaba wajen yin adawa a ƙarƙashin tutar jam’iyyar PDP (wadda ke riƙe da gwamnatin tsakiya). Sai dai a lokacin babu kafafen sadarwa na soshiyal midiya irin yanzu. Hasali ma kila ko da akwai su, ba za a yi adawa ta wuce-wuri da cin mutuncin juna ba irin ta yanzu.

Daga Muhammad Sajo

Abinda aka al’adanta ne cewa wanda ake yi ma adawa idan ya tsima a fagen siyasa, wani sa’ilin yakan iya janye abokan adawarsa su dawo ɓangarensa. Hakan ya faru a lokacin gwamnatin Bafarawa inda ya yi nasarar janye Alhaji Abubakar Shehu Tambuwal ya dawo jam’iyyarsa. Hakan ma ta faru a lokacin Gwamna Aliyu Magatakarda Wamakko inda ya janye Ɗan-Madamin Isa daga wancan ɓangaren na Bafarawa zuwa nasa. Ko a haka da ake yanzu, wa ya san gobe ban da Allah (SWA)? Sarki goma zamani goma. Abinda wani shugaba kan iya jurewa na adawa, wani ba zai ɗauka ba. Kuma inda wani ya yi rawa aka yi mai kari, wani idan ya yi, kashi zai sha. A bayyane take cewa a nan jiharmu ta Sokoto, ana wuce wuri wajen amfani da soshiyal midiya gun yin adawa wadda ta ke da sigar cin zarafi da shiga rigar mutuncin juna har da na iyali. Kuma fa an lura da cewa kowane ɓangare ya sami dama, yi yake, amma ga abinda ya bayyana a halin yanzu, ɗayan ɓangaren na masu adawa ya fi zaƙewa. An tabbatar da cewa a tarihin siyasar Sokoto, ba a yi gwamna mai juriyar sukar adawa ba kamar Barista Aminu Waziri Tambuwal wanda ya sauka jiya-jiya. Me ya sa a Sokoto ba a koyi da salon adawar siyasa ta maƙwabtan jihohinmu na yankin kudu? A tasu salon adawar siyasa, iya sarrafa harshen Turanci da tajwidinsa ko akasin haka ba su ne abin suka ba ga shugaba, sai dai salon jagoranci da wanzar da shiraruwa da ayukka da ke da tasiri ga jama’a, ko bin diddigin ajandar da ɗan takara ya bayyana a lokacin neman ƙuri’un jama’a, da sauransu.

A wani ɓangaren kuma, za a iya cewa, sai bango ya tsage, ƙadangare ke samun kafar shiga. Gwamnatinmu ta Sokoto na buƙatar kimtsa gidanta musamman a haujin sadarwa (media team) saɓanin gwamnatocin da suka gabata na Bafarawa da Wamakko da Tambuwal inda kowaccensu na da gwargwadon ƙwararrin masana masu aiki kafaɗa-da-kafaɗa a haujin rubuta jawabi (speech writing team) da ababen da suka shafi fitar da bayanai (Press release) da aka tantance sosai don kauce ma tuntuɓen alƙalami da saƙo mai harshen damo da sauransu. Idan ko akwai ayarin ƙwararrin masanan (watau media team) to kila ba a ba su cikakkiyar damar yin aiki tare ba don abin ya yi armashi domin kuwa hannu ɗaya ba ya ɗaukar jinƙa.

Idan kuma aka zo ɓangaren ganawa da uban tafiyar, watau Gwamna, nan ma akwai buƙatar gyara sosai. A inda aka fito, lokacin da gwamnatin nan na kan turbar adawa, ganawa da Gwamna Tambuwal na ɗaya daga cikin ƙalubalolin da ake sukarsa da su domin ko komishinoninsa ba su faye samun ganawa da shi ba a lokacin da suke so. Bincike ya tabbatar da cewa duk kanwar ja ce domin babu banbancin jiya da yau inda hasali ma, ko hadiman Gwamna Dokta Ahmad Aliyu mai ci yanzu, shakku suke wajen yi ma mutum iso (ko booking) ɗin ganawa da shi. Sai kuwa idan shi Gwamnan ne ke da buƙata da ganinka. Haka abin ya ke ga muƙarraban gwamnatin, domin kuwa ƙalilan daga ‘yan majalisar Jihar ke da juriyar sauraren jama’arsu a ofis ko a gida kamar yadda ya dace. Wannan ya saɓa ma a ƙalla gwamnoni biyu da aka yi kafin Tambuwal da Ahmad. Domin kuwa ana iya ganawa da Bafarawa a ofis ko gida a wancan lokacin da yake Gwamnan Jihar Sokoto.

ALSO READ [VIEWPOINT] Ex-raying the Pathetic State of the Public Media in Sokoto

Shi Aliyu Wamakko sha-kundum ne domin kusan kowa na iya ganawa da shi a ko ina ta kama sa’ilin da yake gwamna. Ashe kuwa kyawon ɗa ya gadi ubansa. Ai ba kowa ne zai ce sai ya gana da Gwamna ba, sai wanda ke ganin matsayinsa ya kai. Wannan sanken ne ke kawo shakku ga manyan ‘yan bokonmu da sauran masana a Sokoto da ke da zimmar zuwa don bayar da shawara ga Gwamnan ko ‘yan majalisarsa. Akwai ma bayanan da ke nuna cewa galibin komishinonin gwamnatin nan ta Sokoto ba su ɗaukar waya ko da ta wanda suka sani ce. Da fatar za a gyara.

Allah Ya taimaki Jiharmu ta Sokoto, Ya magance muna matsalar tsaro a nan gida da dukkan jihohinmu da ƙasarmu Nijeriya baki ɗaya, amin.

Sajo Dan Jarida ne kuma Malami a Jami’ar Usmanu Danfodiyo Sokoto

Adawar siyasa Jihar Sokoto
Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn WhatsApp Reddit Tumblr Email
Editor
  • Website

Related Posts

World Bank approves $1.25bn loan for Nigeria despite public criticism

July 1, 2026

Why Gbajabiamila shouldn’t be distracted over PFIPC, PEAC controversy – Williams, Olumoro, others

July 1, 2026

NWUS warns prospective students against fake online admission screening portal

June 30, 2026

Leave A Reply Cancel Reply

Naira ends June at ₦1,376/$ despite mid-month swings

July 1, 2026

World Bank approves $1.25bn loan for Nigeria despite public criticism

July 1, 2026

Lagos urges residents to remain calm as flooding persists, approves dredging of 28 drainage channels

July 1, 2026

ADC, 8 other political parties obtain INEC access codes for upload of 2027 candidates [LIST]

July 1, 2026
About Us
About Us

ASHENEWS (AsheNewsDaily.com), published by PenPlus Online Media Publishers, is an independent online newspaper. We report development news, especially on Agriculture, Science, Health and Environment as they affect the under-reported rural and urban poor.

We also conduct investigations, especially in the areas of ASHE, as well as other general interests, including corruption, human rights, illicit financial flows, and politics.

Contact Info:
  • 1st floor, Dogon Daji House, No. 5, Maiduguri Road, Sokoto
  • +234(0)7031140009
  • ashenewsdaily@gmail.com
Facebook Twitter Instagram Pinterest
© 2026 All Rights Reserved. ASHENEWS Daily Designed & Managed By DeedsTech

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.