• Home
  • Agric
  • Sci & Tech
  • Health
  • Environment
  • Hausa News
  • More
    • Business/Banking & Finance
    • POLITICS
    • Entertainments & Sports
    • International
    • Investigation
    • Law & Human Rights
    • Africa
    • ACCOUNTABILITY/CORRUPTION
    • Hassan Gimba
    • Column
    • Prof. Jibrin Ibrahim
    • Prof. M.K. Othman
    • Defense/Security
    • Education
    • Energy/Electricity
    • Entertainment/Arts & Sports
    • Society and Lifestyle
    • Food & Agriculture
    • Health & Healthy Living
    • International News
    • Interviews
    • Investigation/Fact-Check
    • LAW & HUMAN RIGHTS
    • Oil & Gas/Mineral Resources
    • PRESS FREEDOM/JOURNALISM/PR
    • General News
    • Presidency
  • About Us
    • Contact Us
    • Board Of Advisory
    • Privacy Policy
    • Ethics Policy
    • Teamwork And Collaboration Policy
    • Fact-Checking Policy
    • Advertising
  • Media OutReach Newswire
    • Wire News
  • The Stories
Facebook Twitter Instagram
Trending
  • CBN’s new OMO rules to drive rate hold despite cooling inflation, by Hope Moses-Ashike
  • ITC moves to tackle cowpea, sesame export challenges in Benue
  • FG to boost Northeast infrastructure, inaugurates fertility centre in Maiduguri
  • CBN survey: Taxes, insecurity, high interest rates constrain Nigerian firms
  • [VIEWPOINT] A just transition cannot be built on women’s land, labour and bodies,by Dr Melania Chiponda
  • Food inflation rises to 20.31% in July, highest in 10 months
  • Naira strengthens to N1,350/$, strongest level since April
  • DMO allots N1.56trn FGN bonds as demand reaches N1.73trn
Facebook Twitter Instagram YouTube
AsheNewsAsheNews
  • Home
  • Agric

    ITC moves to tackle cowpea, sesame export challenges in Benue

    August 19, 2026

    Food inflation rises to 20.31% in July, highest in 10 months

    August 18, 2026

    Enugu leases 67 tractors to farmers at subsidised rates

    August 18, 2026

    FG reaffirms push for agriculture to curb food shortages

    August 18, 2026

    MUTA urges FG to exclude Benue from ranching pilot

    August 18, 2026
  • Sci & Tech

    FG inaugurates national digital cloud policy

    August 18, 2026

    Nigerian firm deploys AI platform against cybercrime

    August 18, 2026

    Katsina teen gains global recognition for EV design

    August 18, 2026

    Zoho: Businesses risk stalling without structured systems

    August 17, 2026

    Meta, FG launch AI Academy to train Nigerian talents

    August 17, 2026
  • Health

    FG to boost Northeast infrastructure, inaugurates fertility centre in Maiduguri

    August 19, 2026

    WHO: Bundibugyo outbreak in DRC still far from control

    August 18, 2026

    Kano bans IV fluids, blood transfusions at patent medicine stores

    August 18, 2026

    Niger unveils N100m health equipment to strengthen Bida General Hospital

    August 18, 2026

    Nsukka chairman says 20 PHCs nearly complete

    August 18, 2026
  • Environment

    FG reaffirms commitment to secure, credible 2027 elections – Idris

    August 18, 2026

    Niger to host myclimate experts on carbon mission

    August 18, 2026

    Otti congratulates Babangida on 85th birthday

    August 18, 2026

    FCTA moves to tackle flooding in parts of Abuja

    August 17, 2026

    Lagos urges youths to protect ocean, coastal environment

    August 17, 2026
  • Hausa News

    UNA signs MoU to launch air Bissau in Guinea-Bissau

    June 15, 2026

    Otti plans 250-room 5-star hotel in Umuahia

    April 11, 2026

    Anti-quackery task force seals 4 fake hospitals in Rivers

    August 29, 2025

    [BIDIYO] Yadda na lashe gasa ta duniya a fannin Ingilishi – Rukayya ‘yar shekara 17

    August 6, 2025

    A Saka Baki, A Sasanta Saɓani Tsakanin ‘Yanjarida Da Liman, Daga Muhammad Sajo

    May 21, 2025
  • More
    1. Business/Banking & Finance
    2. POLITICS
    3. Entertainments & Sports
    4. International
    5. Investigation
    6. Law & Human Rights
    7. Africa
    8. ACCOUNTABILITY/CORRUPTION
    9. Hassan Gimba
    10. Column
    11. Prof. Jibrin Ibrahim
    12. Prof. M.K. Othman
    13. Defense/Security
    14. Education
    15. Energy/Electricity
    16. Entertainment/Arts & Sports
    17. Society and Lifestyle
    18. Food & Agriculture
    19. Health & Healthy Living
    20. International News
    21. Interviews
    22. Investigation/Fact-Check
    23. LAW & HUMAN RIGHTS
    24. Oil & Gas/Mineral Resources
    25. PRESS FREEDOM/JOURNALISM/PR
    26. General News
    27. Presidency
    Featured
    Recent

    CBN’s new OMO rules to drive rate hold despite cooling inflation, by Hope Moses-Ashike

    August 19, 2026

    ITC moves to tackle cowpea, sesame export challenges in Benue

    August 19, 2026

    FG to boost Northeast infrastructure, inaugurates fertility centre in Maiduguri

    August 19, 2026
  • About Us
    1. Contact Us
    2. Board Of Advisory
    3. Privacy Policy
    4. Ethics Policy
    5. Teamwork And Collaboration Policy
    6. Fact-Checking Policy
    7. Advertising
    Featured
    Recent

    CBN’s new OMO rules to drive rate hold despite cooling inflation, by Hope Moses-Ashike

    August 19, 2026

    ITC moves to tackle cowpea, sesame export challenges in Benue

    August 19, 2026

    FG to boost Northeast infrastructure, inaugurates fertility centre in Maiduguri

    August 19, 2026
  • Media OutReach Newswire
    • Wire News
  • The Stories
AsheNewsAsheNews
Home»General News»[RA’AYI)] Adawar Siyasa A Jihar Sokoto Da Sauran Lamurra
General News

[RA’AYI)] Adawar Siyasa A Jihar Sokoto Da Sauran Lamurra

EditorBy EditorSeptember 6, 2024Updated:September 6, 2024No Comments5 Mins Read
Sokoto-state-map
Share
Facebook Twitter LinkedIn Pinterest Email

Haƙiƙa lamarin jagorancin jama’a a lokacin dimokraɗiyya yana tafiya ne da adawa. Sai dai kuma idan za a yi adawar, ya dace a yi mai ma’ana wadda hankali ke ɗauka. Lallai an yi adawa a lokacin gwamnatin Alhaji Attahiru Ɗalhatu Bafarawa ta APP/ANPP (1999-2003) inda a lokacin, su Hon. Abubakar Shehu Tambuwal da Hon. Arzika Tureta (marigayi) suke a sahun gaba wajen yin adawa a ƙarƙashin tutar jam’iyyar PDP (wadda ke riƙe da gwamnatin tsakiya). Sai dai a lokacin babu kafafen sadarwa na soshiyal midiya irin yanzu. Hasali ma kila ko da akwai su, ba za a yi adawa ta wuce-wuri da cin mutuncin juna ba irin ta yanzu.

Daga Muhammad Sajo

Abinda aka al’adanta ne cewa wanda ake yi ma adawa idan ya tsima a fagen siyasa, wani sa’ilin yakan iya janye abokan adawarsa su dawo ɓangarensa. Hakan ya faru a lokacin gwamnatin Bafarawa inda ya yi nasarar janye Alhaji Abubakar Shehu Tambuwal ya dawo jam’iyyarsa. Hakan ma ta faru a lokacin Gwamna Aliyu Magatakarda Wamakko inda ya janye Ɗan-Madamin Isa daga wancan ɓangaren na Bafarawa zuwa nasa. Ko a haka da ake yanzu, wa ya san gobe ban da Allah (SWA)? Sarki goma zamani goma. Abinda wani shugaba kan iya jurewa na adawa, wani ba zai ɗauka ba. Kuma inda wani ya yi rawa aka yi mai kari, wani idan ya yi, kashi zai sha. A bayyane take cewa a nan jiharmu ta Sokoto, ana wuce wuri wajen amfani da soshiyal midiya gun yin adawa wadda ta ke da sigar cin zarafi da shiga rigar mutuncin juna har da na iyali. Kuma fa an lura da cewa kowane ɓangare ya sami dama, yi yake, amma ga abinda ya bayyana a halin yanzu, ɗayan ɓangaren na masu adawa ya fi zaƙewa. An tabbatar da cewa a tarihin siyasar Sokoto, ba a yi gwamna mai juriyar sukar adawa ba kamar Barista Aminu Waziri Tambuwal wanda ya sauka jiya-jiya. Me ya sa a Sokoto ba a koyi da salon adawar siyasa ta maƙwabtan jihohinmu na yankin kudu? A tasu salon adawar siyasa, iya sarrafa harshen Turanci da tajwidinsa ko akasin haka ba su ne abin suka ba ga shugaba, sai dai salon jagoranci da wanzar da shiraruwa da ayukka da ke da tasiri ga jama’a, ko bin diddigin ajandar da ɗan takara ya bayyana a lokacin neman ƙuri’un jama’a, da sauransu.

A wani ɓangaren kuma, za a iya cewa, sai bango ya tsage, ƙadangare ke samun kafar shiga. Gwamnatinmu ta Sokoto na buƙatar kimtsa gidanta musamman a haujin sadarwa (media team) saɓanin gwamnatocin da suka gabata na Bafarawa da Wamakko da Tambuwal inda kowaccensu na da gwargwadon ƙwararrin masana masu aiki kafaɗa-da-kafaɗa a haujin rubuta jawabi (speech writing team) da ababen da suka shafi fitar da bayanai (Press release) da aka tantance sosai don kauce ma tuntuɓen alƙalami da saƙo mai harshen damo da sauransu. Idan ko akwai ayarin ƙwararrin masanan (watau media team) to kila ba a ba su cikakkiyar damar yin aiki tare ba don abin ya yi armashi domin kuwa hannu ɗaya ba ya ɗaukar jinƙa.

Idan kuma aka zo ɓangaren ganawa da uban tafiyar, watau Gwamna, nan ma akwai buƙatar gyara sosai. A inda aka fito, lokacin da gwamnatin nan na kan turbar adawa, ganawa da Gwamna Tambuwal na ɗaya daga cikin ƙalubalolin da ake sukarsa da su domin ko komishinoninsa ba su faye samun ganawa da shi ba a lokacin da suke so. Bincike ya tabbatar da cewa duk kanwar ja ce domin babu banbancin jiya da yau inda hasali ma, ko hadiman Gwamna Dokta Ahmad Aliyu mai ci yanzu, shakku suke wajen yi ma mutum iso (ko booking) ɗin ganawa da shi. Sai kuwa idan shi Gwamnan ne ke da buƙata da ganinka. Haka abin ya ke ga muƙarraban gwamnatin, domin kuwa ƙalilan daga ‘yan majalisar Jihar ke da juriyar sauraren jama’arsu a ofis ko a gida kamar yadda ya dace. Wannan ya saɓa ma a ƙalla gwamnoni biyu da aka yi kafin Tambuwal da Ahmad. Domin kuwa ana iya ganawa da Bafarawa a ofis ko gida a wancan lokacin da yake Gwamnan Jihar Sokoto.

ALSO READ [VIEWPOINT] Ex-raying the Pathetic State of the Public Media in Sokoto

Shi Aliyu Wamakko sha-kundum ne domin kusan kowa na iya ganawa da shi a ko ina ta kama sa’ilin da yake gwamna. Ashe kuwa kyawon ɗa ya gadi ubansa. Ai ba kowa ne zai ce sai ya gana da Gwamna ba, sai wanda ke ganin matsayinsa ya kai. Wannan sanken ne ke kawo shakku ga manyan ‘yan bokonmu da sauran masana a Sokoto da ke da zimmar zuwa don bayar da shawara ga Gwamnan ko ‘yan majalisarsa. Akwai ma bayanan da ke nuna cewa galibin komishinonin gwamnatin nan ta Sokoto ba su ɗaukar waya ko da ta wanda suka sani ce. Da fatar za a gyara.

Allah Ya taimaki Jiharmu ta Sokoto, Ya magance muna matsalar tsaro a nan gida da dukkan jihohinmu da ƙasarmu Nijeriya baki ɗaya, amin.

Sajo Dan Jarida ne kuma Malami a Jami’ar Usmanu Danfodiyo Sokoto

Adawar siyasa Jihar Sokoto
Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn WhatsApp Reddit Tumblr Email
Editor
  • Website

Related Posts

FG, states, LGCs share N3.007trn FAAC allocation

August 18, 2026

Evangelist Ojo-Peters launches foundation to aid the less privileged

August 17, 2026

Ujah wins Presidential Distinguished Civil Service Career award

August 16, 2026

Leave A Reply Cancel Reply

CBN’s new OMO rules to drive rate hold despite cooling inflation, by Hope Moses-Ashike

August 19, 2026

ITC moves to tackle cowpea, sesame export challenges in Benue

August 19, 2026

FG to boost Northeast infrastructure, inaugurates fertility centre in Maiduguri

August 19, 2026

CBN survey: Taxes, insecurity, high interest rates constrain Nigerian firms

August 18, 2026
About Us
About Us

ASHENEWS (AsheNewsDaily.com), published by PenPlus Online Media Publishers, is an independent online newspaper. We report development news, especially on Agriculture, Science, Health and Environment as they affect the under-reported rural and urban poor.

We also conduct investigations, especially in the areas of ASHE, as well as other general interests, including corruption, human rights, illicit financial flows, and politics.

Contact Info:
  • 1st floor, Dogon Daji House, No. 5, Maiduguri Road, Sokoto
  • +234(0)7031140009
  • ashenewsdaily@gmail.com
Facebook Twitter Instagram Pinterest
© 2026 All Rights Reserved. ASHENEWS Daily Designed & Managed By DeedsTech

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.