• Home
  • Agric
  • Sci & Tech
  • Health
  • Environment
  • Hausa News
  • More
    • Business/Banking & Finance
    • POLITICS
    • Entertainments & Sports
    • International
    • Investigation
    • Law & Human Rights
    • Africa
    • ACCOUNTABILITY/CORRUPTION
    • Hassan Gimba
    • Column
    • Prof. Jibrin Ibrahim
    • Prof. M.K. Othman
    • Defense/Security
    • Education
    • Energy/Electricity
    • Entertainment/Arts & Sports
    • Society and Lifestyle
    • Food & Agriculture
    • Health & Healthy Living
    • International News
    • Interviews
    • Investigation/Fact-Check
    • LAW & HUMAN RIGHTS
    • Oil & Gas/Mineral Resources
    • PRESS FREEDOM/JOURNALISM/PR
    • General News
    • Presidency
  • About Us
    • Contact Us
    • Board Of Advisory
    • Privacy Policy
    • Ethics Policy
    • Teamwork And Collaboration Policy
    • Fact-Checking Policy
    • Advertising
  • Media OutReach Newswire
    • Wire News
  • The Stories
Facebook Twitter Instagram
Trending
  • Naira strengthens to N1,367.76/$ as dollar liquidity improves
  • Ex-ECOWAS Court President Asante nominated for Ghana’s Supreme Court
  • US imposes new tariffs on Nigeria, 59 other countries [FULL LIST]
  • Naira strengthens against Euro to N1,557 as FX market stability persists
  • BUA Cement H1 profit jumps 79% to N384.44bn as earnings surge
  • Kano health commissioner urges farmers to boost nutritious food production
  • UNDP/GEF-SGP empowers over 600 nature-positive MSMEs
  • Ogun VCDP distributes 16 tricycles to farmer groups
Facebook Twitter Instagram YouTube
AsheNewsAsheNews
  • Home
  • Agric

    Kano health commissioner urges farmers to boost nutritious food production

    July 24, 2026

    Ogun VCDP distributes 16 tricycles to farmer groups

    July 24, 2026

    JAMB announces alternative admission process for NCE, agric courses

    July 23, 2026

    Edo farmers benefit as Tinubu’s fertilizer programme launches

    July 23, 2026

    Nigeria unveils digital platform to boost plant disease surveillance in West, Central Africa

    July 23, 2026
  • Sci & Tech

    NASENI shortlists 12 research proposals for commercialisation grant

    July 24, 2026

    TikTok removes 4.8m videos in Nigeria in Q1 2026

    July 23, 2026

    ALTON: Nigeria’s digital economy ambition unattainable without protected telecom infrastructure

    July 23, 2026

    Nokia reports strong Q2 2026 results on AI demand

    July 23, 2026

    Nigeria, ITU urge African unity on global digital governance

    July 23, 2026
  • Health

    Edo unveils roadmap for universal health coverage

    July 24, 2026

    NAFDAC launches nationwide crackdown on sachet, small-bottle alcohol

    July 23, 2026

    Neurologist warns: Pollution threatens brain health

    July 23, 2026

    Anti-ritual killing advocate expands nationwide campaign

    July 23, 2026

    Claudia Sanso-Olu, Oshodi-Isolo chairman flag off 2026 MNCAH+N week

    July 23, 2026
  • Environment

    UNDP/GEF-SGP empowers over 600 nature-positive MSMEs

    July 24, 2026

    Association to deliver 10,000 social housing units by 2030

    July 24, 2026

    NSIB probes runway excursion at Benin airport

    July 24, 2026

    CSOs launch forest, climate journalism fellowship to deepen environmental reporting in Nigeria

    July 23, 2026

    NDE launches online registration for phase III of renewed hope employment initiative

    July 23, 2026
  • Hausa News

    UNA signs MoU to launch air Bissau in Guinea-Bissau

    June 15, 2026

    Otti plans 250-room 5-star hotel in Umuahia

    April 11, 2026

    Anti-quackery task force seals 4 fake hospitals in Rivers

    August 29, 2025

    [BIDIYO] Yadda na lashe gasa ta duniya a fannin Ingilishi – Rukayya ‘yar shekara 17

    August 6, 2025

    A Saka Baki, A Sasanta Saɓani Tsakanin ‘Yanjarida Da Liman, Daga Muhammad Sajo

    May 21, 2025
  • More
    1. Business/Banking & Finance
    2. POLITICS
    3. Entertainments & Sports
    4. International
    5. Investigation
    6. Law & Human Rights
    7. Africa
    8. ACCOUNTABILITY/CORRUPTION
    9. Hassan Gimba
    10. Column
    11. Prof. Jibrin Ibrahim
    12. Prof. M.K. Othman
    13. Defense/Security
    14. Education
    15. Energy/Electricity
    16. Entertainment/Arts & Sports
    17. Society and Lifestyle
    18. Food & Agriculture
    19. Health & Healthy Living
    20. International News
    21. Interviews
    22. Investigation/Fact-Check
    23. LAW & HUMAN RIGHTS
    24. Oil & Gas/Mineral Resources
    25. PRESS FREEDOM/JOURNALISM/PR
    26. General News
    27. Presidency
    Featured
    Recent

    Naira strengthens to N1,367.76/$ as dollar liquidity improves

    July 24, 2026

    Ex-ECOWAS Court President Asante nominated for Ghana’s Supreme Court

    July 24, 2026

    US imposes new tariffs on Nigeria, 59 other countries [FULL LIST]

    July 24, 2026
  • About Us
    1. Contact Us
    2. Board Of Advisory
    3. Privacy Policy
    4. Ethics Policy
    5. Teamwork And Collaboration Policy
    6. Fact-Checking Policy
    7. Advertising
    Featured
    Recent

    Naira strengthens to N1,367.76/$ as dollar liquidity improves

    July 24, 2026

    Ex-ECOWAS Court President Asante nominated for Ghana’s Supreme Court

    July 24, 2026

    US imposes new tariffs on Nigeria, 59 other countries [FULL LIST]

    July 24, 2026
  • Media OutReach Newswire
    • Wire News
  • The Stories
AsheNewsAsheNews
Home»General News»[RA’AYI)] Adawar Siyasa A Jihar Sokoto Da Sauran Lamurra
General News

[RA’AYI)] Adawar Siyasa A Jihar Sokoto Da Sauran Lamurra

EditorBy EditorSeptember 6, 2024Updated:September 6, 2024No Comments5 Mins Read
Sokoto-state-map
Share
Facebook Twitter LinkedIn Pinterest Email

Haƙiƙa lamarin jagorancin jama’a a lokacin dimokraɗiyya yana tafiya ne da adawa. Sai dai kuma idan za a yi adawar, ya dace a yi mai ma’ana wadda hankali ke ɗauka. Lallai an yi adawa a lokacin gwamnatin Alhaji Attahiru Ɗalhatu Bafarawa ta APP/ANPP (1999-2003) inda a lokacin, su Hon. Abubakar Shehu Tambuwal da Hon. Arzika Tureta (marigayi) suke a sahun gaba wajen yin adawa a ƙarƙashin tutar jam’iyyar PDP (wadda ke riƙe da gwamnatin tsakiya). Sai dai a lokacin babu kafafen sadarwa na soshiyal midiya irin yanzu. Hasali ma kila ko da akwai su, ba za a yi adawa ta wuce-wuri da cin mutuncin juna ba irin ta yanzu.

Daga Muhammad Sajo

Abinda aka al’adanta ne cewa wanda ake yi ma adawa idan ya tsima a fagen siyasa, wani sa’ilin yakan iya janye abokan adawarsa su dawo ɓangarensa. Hakan ya faru a lokacin gwamnatin Bafarawa inda ya yi nasarar janye Alhaji Abubakar Shehu Tambuwal ya dawo jam’iyyarsa. Hakan ma ta faru a lokacin Gwamna Aliyu Magatakarda Wamakko inda ya janye Ɗan-Madamin Isa daga wancan ɓangaren na Bafarawa zuwa nasa. Ko a haka da ake yanzu, wa ya san gobe ban da Allah (SWA)? Sarki goma zamani goma. Abinda wani shugaba kan iya jurewa na adawa, wani ba zai ɗauka ba. Kuma inda wani ya yi rawa aka yi mai kari, wani idan ya yi, kashi zai sha. A bayyane take cewa a nan jiharmu ta Sokoto, ana wuce wuri wajen amfani da soshiyal midiya gun yin adawa wadda ta ke da sigar cin zarafi da shiga rigar mutuncin juna har da na iyali. Kuma fa an lura da cewa kowane ɓangare ya sami dama, yi yake, amma ga abinda ya bayyana a halin yanzu, ɗayan ɓangaren na masu adawa ya fi zaƙewa. An tabbatar da cewa a tarihin siyasar Sokoto, ba a yi gwamna mai juriyar sukar adawa ba kamar Barista Aminu Waziri Tambuwal wanda ya sauka jiya-jiya. Me ya sa a Sokoto ba a koyi da salon adawar siyasa ta maƙwabtan jihohinmu na yankin kudu? A tasu salon adawar siyasa, iya sarrafa harshen Turanci da tajwidinsa ko akasin haka ba su ne abin suka ba ga shugaba, sai dai salon jagoranci da wanzar da shiraruwa da ayukka da ke da tasiri ga jama’a, ko bin diddigin ajandar da ɗan takara ya bayyana a lokacin neman ƙuri’un jama’a, da sauransu.

A wani ɓangaren kuma, za a iya cewa, sai bango ya tsage, ƙadangare ke samun kafar shiga. Gwamnatinmu ta Sokoto na buƙatar kimtsa gidanta musamman a haujin sadarwa (media team) saɓanin gwamnatocin da suka gabata na Bafarawa da Wamakko da Tambuwal inda kowaccensu na da gwargwadon ƙwararrin masana masu aiki kafaɗa-da-kafaɗa a haujin rubuta jawabi (speech writing team) da ababen da suka shafi fitar da bayanai (Press release) da aka tantance sosai don kauce ma tuntuɓen alƙalami da saƙo mai harshen damo da sauransu. Idan ko akwai ayarin ƙwararrin masanan (watau media team) to kila ba a ba su cikakkiyar damar yin aiki tare ba don abin ya yi armashi domin kuwa hannu ɗaya ba ya ɗaukar jinƙa.

Idan kuma aka zo ɓangaren ganawa da uban tafiyar, watau Gwamna, nan ma akwai buƙatar gyara sosai. A inda aka fito, lokacin da gwamnatin nan na kan turbar adawa, ganawa da Gwamna Tambuwal na ɗaya daga cikin ƙalubalolin da ake sukarsa da su domin ko komishinoninsa ba su faye samun ganawa da shi ba a lokacin da suke so. Bincike ya tabbatar da cewa duk kanwar ja ce domin babu banbancin jiya da yau inda hasali ma, ko hadiman Gwamna Dokta Ahmad Aliyu mai ci yanzu, shakku suke wajen yi ma mutum iso (ko booking) ɗin ganawa da shi. Sai kuwa idan shi Gwamnan ne ke da buƙata da ganinka. Haka abin ya ke ga muƙarraban gwamnatin, domin kuwa ƙalilan daga ‘yan majalisar Jihar ke da juriyar sauraren jama’arsu a ofis ko a gida kamar yadda ya dace. Wannan ya saɓa ma a ƙalla gwamnoni biyu da aka yi kafin Tambuwal da Ahmad. Domin kuwa ana iya ganawa da Bafarawa a ofis ko gida a wancan lokacin da yake Gwamnan Jihar Sokoto.

ALSO READ [VIEWPOINT] Ex-raying the Pathetic State of the Public Media in Sokoto

Shi Aliyu Wamakko sha-kundum ne domin kusan kowa na iya ganawa da shi a ko ina ta kama sa’ilin da yake gwamna. Ashe kuwa kyawon ɗa ya gadi ubansa. Ai ba kowa ne zai ce sai ya gana da Gwamna ba, sai wanda ke ganin matsayinsa ya kai. Wannan sanken ne ke kawo shakku ga manyan ‘yan bokonmu da sauran masana a Sokoto da ke da zimmar zuwa don bayar da shawara ga Gwamnan ko ‘yan majalisarsa. Akwai ma bayanan da ke nuna cewa galibin komishinonin gwamnatin nan ta Sokoto ba su ɗaukar waya ko da ta wanda suka sani ce. Da fatar za a gyara.

Allah Ya taimaki Jiharmu ta Sokoto, Ya magance muna matsalar tsaro a nan gida da dukkan jihohinmu da ƙasarmu Nijeriya baki ɗaya, amin.

Sajo Dan Jarida ne kuma Malami a Jami’ar Usmanu Danfodiyo Sokoto

Adawar siyasa Jihar Sokoto
Share. Facebook Twitter Pinterest LinkedIn WhatsApp Reddit Tumblr Email
Editor
  • Website

Related Posts

JAMB announces alternative admission process for NCE, agric courses

July 23, 2026

Dangote Refinery raises $2.5bn in private equity placement

July 23, 2026

Atiku faults Tinubu over N22.15bn allocation for traditional rulers’ palaces

July 23, 2026

Leave A Reply Cancel Reply

Naira strengthens to N1,367.76/$ as dollar liquidity improves

July 24, 2026

Ex-ECOWAS Court President Asante nominated for Ghana’s Supreme Court

July 24, 2026

US imposes new tariffs on Nigeria, 59 other countries [FULL LIST]

July 24, 2026

Naira strengthens against Euro to N1,557 as FX market stability persists

July 24, 2026
About Us
About Us

ASHENEWS (AsheNewsDaily.com), published by PenPlus Online Media Publishers, is an independent online newspaper. We report development news, especially on Agriculture, Science, Health and Environment as they affect the under-reported rural and urban poor.

We also conduct investigations, especially in the areas of ASHE, as well as other general interests, including corruption, human rights, illicit financial flows, and politics.

Contact Info:
  • 1st floor, Dogon Daji House, No. 5, Maiduguri Road, Sokoto
  • +234(0)7031140009
  • ashenewsdaily@gmail.com
Facebook Twitter Instagram Pinterest
© 2026 All Rights Reserved. ASHENEWS Daily Designed & Managed By DeedsTech

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.